Babban Bankin Najeriya Ya karyata zan zai Canja Kuɗaɗen kasar

Babban bankin Najeriya na jan hankalin al’ummar kasar kan cewa sakon dake yawo a kafafen sada zumunta da wasu jiridu cewar za a canja Kudaden kasar ba gaskiya bane, kazon gizo ne kawai   Don haka babban bankin ya ke jan hankalin ku da kuyi watsi da wannan zancen, babu kamshin gaskiya cikinsa.     … Read more

Faɗa Ko Gasar Technology Tsakanin China Da America

Me yake faruwa tsakanin America (iPhone 15 Pro Max) da kuma ‘kasar China (Huwaie Meta 60 Pro Max)? _____________________________ Jiya Talata Kamfanin Apple 🍎 dake ‘kera wayoyin iPhone a America ya fitar da sabuwar wayar iPhone 15, mafi tsada a Tarihin wayoyin Kamfanin na Apple a jerin iPhone, akan Farashin 0.031 Bitcoin, ko Dala dubu … Read more

Ana Shirin Tsige Shugaban Kasar America Joe Biden

Shugaban Majalisar Wakilan Amurka ya ce Majalisar za ta ƙaddamar da bincike kan batun tsige shugaba Joe Biden a hukumance.   Kevin McCarthy ya ce binciken zai mayar da hankali ne kan zarge-zargen “saɓa ƙa’idar aiki, kawo cikas wurin aiki da kuma rashawa.”   Ƴan majalisa na jam’iyyar Republican sun kwashe lokaci suna bincike kan … Read more

Allah Ya Yiwa Hajiya Farida Sani Ɗiso Rasùwa, Tsohuwar Matar Sarkin Daura Wacce Akafi Sani Da Giwar Sarkin Daura.

INNÀ LILLAHÍ WA’INNÀ ILAIHÍ RAJI’ÙN.   Masarautan Daura Tayi Rashi.   Allah Ya Yiwa Hajiya Farida Sani Ɗiso Rasùwa, Tsohuwar Matar Sarkin Daura Wacce Akafi Sani Da Giwar Sarkin Daura.   Muna mika sakon ta’azziya ga daukacin al’ummar musulmai musamman masaraukan Daura bisa wannan rashi.   Allah Ya Jikanta Da Rahama. Amin

Hon, Mannir Babba Ɗan Agundi Yayi Nasara A Kotu Inda Ta Tabbatar Masa Da Kujeran Sa.

DA DUMI DUMIN SA:   Kotu Ta Tabbatar Da Nasarar Mannir Babba Ɗan Agundi A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaɓen Ɗan Majalisar Tarayya Mai Wakiltar Karamar Hukumar Kumbotso Dake Kano.   Kotun ta yanke shari’ar ne a yau litinin 11/09/2023, bayan samun sahihan hujjoji daga wanda ake tuhuma. Inda ta tabbatar wa da Mannir a … Read more

An Kama Bama Bamai Guda 399 NDLEA

Jami’an hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya, NDLEA sun ce sun kama bama-bamai kimanin 399 daga hannun wani mutum a kan hanyar Mokwa-Jebba a ranar 7 ga watan Satumba.   Hukumar ta ce ta damƙa mutumin da ake zargi mai shekara 39 ga hukumomin soji a jihar da abin ya faru wato … Read more

Masu Tonon Ma’adanai 30 sun Mutu Bayan Ruftawar Kasa

Masu haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba 30 ne suka mutu bayan ƙasa ta rufta kansu a ƙaramar hukumar Kuje da ke Abuja babban birnin Najeriya. Shugaban ƙaramar hukumar ne ya bayyana haka ranar Alhamis a lokacin da shugabannin ƙananan hukumomin birnin suka gana da ministan Abuja, Nyesom Wike. Haka kuma masu garkuwa da mutane … Read more