Labarai

Su wane ne kusoshin gwamnatin Tinubu?

Su wane ne kusoshin gwamnatin Tinubu?

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya rantsar da ministocinsa a ranar Litinin, kimanin wata uku bayan kama aiki.

 

Majalisar ministocin mai ƙunshe da mutum 45 na cike da tsofaffin gwamnoni da ƴan majalisar dokoki.

 

Kimanin rabin ministocin tsofaffin gwamnoni ne da tsofaffin ƴan majalisa.

 

Majalisar ministocin kuma ta ƙunshi ƙwararru daga ɓangarori da dama, kamar lafiya da fasahar sadarwar zamani.

APPLY NOW!  Masu Tonon Ma'adanai 30 sun Mutu Bayan Ruftawar Kasa

 

Shugaban ƙasar ya kuma ci gaba da ministoci biyu daga tsohuwar gwamnatin magabacinsa Muhammadu Buhari, wato Heineken Lokpobiri da Festus Keyamo.

 

Kamar sauran gwamnatocin baya, ban da ta Goodluck Jonathan, mata ba su samu abin da ya kai kashi 20 cikin ɗari na muƙaman ministocin ba.

 

Ga bayani game da sabbin jiga-jigan gwamnatin Tinubu da kuma rawar da za su iya takawa.

APPLY NOW!  Shugaban ECOWAS bola Tinubu ya sakawa Nijar Dokoki