An rataye mutum uku da suka kai harin bam da ya kashe sama da mutum 300

Kasar Iraqi ta rataye wasu mutum uku da aka samu da hannu a harin bam da aka kai a birnin Bagadaza.

 

Kasar Iraƙi ta rataye wasu mutum uku da aka samu da hannu a harin bam da aka kai a birnin Bagadaza.

 

Wannan harin bam ya faru ne a cikin shakarar 2016 a cikin watan azumi kuma ya kashe mutane sama da 300 tare da jikkata wasu da dama.

 

Wannan dai shi ne harin bam mafi muni da aka kai a Iraki tun bayan mamayar da Amurka ta yi a shekara ta 2003.

 

An aiwatar da hukuncin kisan ne a ranar Lahadi ko Litinin, in ji ofishin Firayim Minista Mohammed Shia al-Sudani.

 

Amma dai ba a bayyana sunayen wadanda aka kashe ba.

 

Firaministan ƙasar ya shaida wa iyalan wadanda abin ya shafa cewa an zartar da hukuncin kisa kan mutanen da ke da hannu a tashin bam din.

See Also  Yadda zai faru idan aka kwace kujeran Gwamna a Kotun Gaba